1, Mummunan harin da ƴanbidiga suka kai wa wasu masallata a masallacin jihar Katsina tare da kashe masu ibada na ci gaba da tayar da hankali a Najeriya.
Maharan sun far wa masallatan a lokacin da suke tsaka da sallar asuba a garin Unguwar Mantau cikin ƙaramar hukumar Malumfashi tare da buɗe musu wuta.
Harin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 28 tare da jikkatar wasu da dama.
Wasu garuruwan yankunan arewa maso yammacin Najeriya na fama da hare-haren ƴanbindiga waɗanda a wasu lotukan kan tilasta wa mazauna garuruwa da ƙauyuka tserewa.
Tags
labaran Duniya